Gwamnoni na duba yiwuwar karbe ragamar tallafin man fetur daga NNPC


Majalisar tattalin arziki NEC da ta kunshi jihohi 36 na Najeriya, ta yi barazanar za ta karbe ragamar tafiyar da tallafin man fetur ganin irin biliyoyin dala da NNPC ke kashewa a shekara.

Shugaban majalisar Gwamna Abdulazeez Yari na jihar Zamfara ya shaida wa manema labarai jim kadan bayan fitowarsu daga taron na NEC wanda mataimakin shubgaban kasa Yemi Osinbajo ya jagoranta ranar Alhamis a Abuja. 


Ya kara da cewa Gwamnonin za su sake zama a kan lamarin a watan Yuni domin duba yiwuwar ko za su karbi ragamar tallafin man fetur daga NNPC wacce take kashe Naira biliyan 800 a kowane shekara.

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN