Type Here to Get Search Results !

Bagudu ya bukaci a inganta yadda ake amfani da Facebook - ISYAKU.COM

Gwamna Atiku Bagudu na jihar Kebbi ya ce ba daidai bane ma'abuta amfani da Facebook su dinga amfani da wannan kafar domin mayar da shi wata kafa ta yanke hukunci daga jama'a a kan ayyuka tare da kudirorin gwaamnati yayin da ake cikin yin su kafin a kammala su.

Gwamnan ya yi wannan jawabi ne ranar Talata a dakin taro na masaukin shugaban kasa a Birnin kebbi yayin da ya halarci wani taro da wata kungiyar matasa ta shirya kan murnar cika shekara 19 na komawa mulkin Dimokradiyya a jihar Kebbi.

Gwamnan ya bayyana cewa "wasu mutane sun mayar da Facebook zauren jin ra'ayin jama'a a kan ayyuka tare da manufofin gwamnati da ake yi".

Ya kara da cewa babu yadda za a yi a sami cikakken bayani a kan wadannan ayyuka domin ana cikin yin su ne ba a kammala ba, amma sai masu amfani da Facebook su yanke hukunci .

Bagudu ya bukaci a tsabtace yadda ake amfani da Facebook domin ganin an sami tsari ingantacce na samar da bayanai masu tsabta tare da sada zumunci.

Daga Isyaku Garba

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN