Amurka ta fitar da sabbin bukatunta kan yarjejeniyar Nukiliya da Iran

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Mike Pompeo ya fitar da jerin sabbin bukatun da kasarsa ta ke so a amince da su don sake kulla yarjejeniyar Nukiliya da Iran wadda Donald Trump ya ce sun janye daga cikinta.

A jawabinsa na farko da ya yi, Pompeo ya yi wa Iran barazana da takunkumai mafiya tsauria cikin tarihi.

Ya ce, sabbin takunkuman da za su saka wa Iran suna da tsauri sosai, kuma idan Kasar ta ki sauya manufofinta a Gabas ta Tsakiya to Trump zai bullo mata ta bayan gida.

Pompeo ya bayyana cewa, Iran ta kasance tana yakar dukkan Kasashen Gabas ta Tsakiya kuma idan sabbin takunkuman Amurka suka zo to Iran za ta koma aiyukan neman farfado da tattalin arzikinta. 
Ya ce, za su takurawa Iran ta yi sabon tsari na ko dai ta daina yaki a Gabas ta tsakiya ko kuma ta ci gaba da asarar kudadenta a kasashen waje.

Ministan ya ci gabada cewa, idan Iran ta sauya halayyarta to Amurka za ta dawo da alakar kasuwanci da diplomasiyya da ita tare da ba ta damar habaka fasaharta ta kere-kere.

Pompeo ya gargadi kasashen Turai da ke son ci gaba da amfani da yarjejeniyar Nukiliya da Iran inda ya ce, hakan zai sanya Amurka daukan matakan ba sani ba sabo.

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

#TRT
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN