Yar yi wa kasa hidima NYSC ta gurfana a gaban Kotu bisa zargin cin amana

Hukumar EFCC a jihar Gombe ta gurfanar da wata mai yi ma kasa hidima NYSC a gaban Justice Abubakar Jauro na babban Kotun tarayya bisa zargin cin amana da yin karya domin a karbi kudi.

Wannan ya biyo bayan wata takardar koke da wani Yusuf Idris ya rubuta wa hukumar bisa lamarin mazauni rukunin gidaje na Tumfure da ke Gombe.

Takardar koken ta ce  ranar 21 ga watan Maris 2017 wacce ake zargin tare da wasu mutane da suka tsere ta karbi N63.000.00 daga hannunsa da niyyar cewa za su sama mashi aiki a hukumar  Kwastam NCS amma suka kasa tabbatar da haka kuma kudinsa suka makale.

Bayanai sun nuna cewa an saka kudin ne a asusun ajiya na Banki wanda ke dauke da sunan Maduako Ugonma Chinomso a Bankin Union Bank Gombe mai lamba 0053158443.

 Bayan an karanto mata zargii da ake yi mata, wacce ake zargin bata amsa laifin ta ba sakamakon haka Justice Jauro ya dage sauraron shari'ar har zuwa ranar 16 ga watan Afrilu domin ci gaba da shari'ar yain da aka tasa keyarta zuwa Kurkuku kafin lokacin zaman Kotu na gaba.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN