Type Here to Get Search Results !

Main event

Yadda aka sace Limamin Masallacin Senchi

Limamin Masallacin Juma'a na Senchi Alh Mande Kibiya dattijo ne da ya gamu da ibtila'i na masu sace mutane domin su karbi kudin fansa.
Amma wani bincike da muka gudanar ya nuna cewa wadanda suka sace shi wasu yara ne al'ummar Fulani wadanda suka san daji matuka kuma wannan shi ne karo na biyu da aka sace shi .

Haka zalika bayanai sun nuna cewa bayan da aka sace shi daga gidansa a garin Kibiya an kai shi wani daji ne a cikin jihar Zamfara.

Jihar Zamfara dai ta zama matattara ga ayyukan garkuwa da mutane da harkar ta'addanci na kisan bayin Allah da basu ji kuma basu gani ba.

Amma yanzu haka mahukunta sun dauki tsattsaran matakan tsaro a jihar Zamfara domin ganin an shawo kan irin ayyukan ta'addanci da suka auku a baya.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies