Hukumar da ke kula da hanyoyin gwamnatin tarayya a Najeriya reshen jihar Kebbi FERMA ta ce ta fara gyara hanyoyin da suka lalace na gwamnatin tarayya a garin Argungu, Ribah da Arewa da kuma hanyar jami'ar tarayya a Birnin kebbi.
Shugaban hukumar na reshen jihar Kebbi Riwanu Usman ya shaida wa wakilin kamfanin dillancin labarai na Najeriya yayin da yake zantawa da shi ranar Juma'a a Birnin kebbi.
Ya ce hukumar ta dukufa domin ganin ta gyara hanyoyin da suka lalace wanda ya hada da yin ciko a wajen da hanya ta fashe tare da cika ramu a hanyoyin .
Haka zalika ya ce hukumar ta kammala hanya mai tsawon kilomita 2.5 a jami'ar tarayya Birnin kebbi da kuma hanya mai tsawon mita 14 a Dirin Daji
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Shugaban hukumar na reshen jihar Kebbi Riwanu Usman ya shaida wa wakilin kamfanin dillancin labarai na Najeriya yayin da yake zantawa da shi ranar Juma'a a Birnin kebbi.
Ya ce hukumar ta dukufa domin ganin ta gyara hanyoyin da suka lalace wanda ya hada da yin ciko a wajen da hanya ta fashe tare da cika ramu a hanyoyin .
Haka zalika ya ce hukumar ta kammala hanya mai tsawon kilomita 2.5 a jami'ar tarayya Birnin kebbi da kuma hanya mai tsawon mita 14 a Dirin Daji
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Tags:
BIRNIN-KEBBI