Type Here to Get Search Results !

FERMA ta fara gyara wasu hanyoyin mota a jihar Kebbi

Hukumar da ke kula da hanyoyin gwamnatin tarayya a Najeriya reshen jihar Kebbi FERMA ta ce ta fara gyara hanyoyin da suka lalace na gwamnatin tarayya a garin Argungu, Ribah da Arewa da kuma hanyar jami'ar tarayya a Birnin kebbi.

Shugaban hukumar na reshen jihar Kebbi Riwanu Usman ya shaida wa wakilin kamfanin dillancin labarai na Najeriya yayin da yake zantawa da shi ranar Juma'a a Birnin kebbi.

Ya ce hukumar ta dukufa domin ganin ta gyara hanyoyin da suka lalace wanda ya hada da yin ciko a wajen da hanya ta fashe tare da cika ramu a hanyoyin .

Haka zalika  ya ce hukumar ta kammala hanya mai tsawon kilomita 2.5 a jami'ar tarayya Birnin kebbi da kuma hanya mai tsawon mita 14 a Dirin Daji 


Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN