FERMA ta fara gyara wasu hanyoyin mota a jihar Kebbi

Hukumar da ke kula da hanyoyin gwamnatin tarayya a Najeriya reshen jihar Kebbi FERMA ta ce ta fara gyara hanyoyin da suka lalace na gwamnatin tarayya a garin Argungu, Ribah da Arewa da kuma hanyar jami'ar tarayya a Birnin kebbi.

Shugaban hukumar na reshen jihar Kebbi Riwanu Usman ya shaida wa wakilin kamfanin dillancin labarai na Najeriya yayin da yake zantawa da shi ranar Juma'a a Birnin kebbi.

Ya ce hukumar ta dukufa domin ganin ta gyara hanyoyin da suka lalace wanda ya hada da yin ciko a wajen da hanya ta fashe tare da cika ramu a hanyoyin .

Haka zalika  ya ce hukumar ta kammala hanya mai tsawon kilomita 2.5 a jami'ar tarayya Birnin kebbi da kuma hanya mai tsawon mita 14 a Dirin Daji 


Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN