Yadda aka dambace tsakanin soji, yansanda da jami'an FRSC a Abuja.

Bayanai daga birnin Abuja sun nuna cewa an sami hatsaniya tsakanin Sojoji, yansanda da kuma jami'an kiyaye hadurra na kasa FRSC, bayanai sun nuna cewa matsalar ta taso ne bayan yansanda da ke aiki da AEPB suka yi kokarin bayar da takarda a hukumnance ga ofishin FRSC da ke Wuse zone 7.

Rahotanni sun yi zargin cewa soji da yansanda da ke aiki da AEPB sun dan lallasa wata jami'ar FRSC wanda ya haddasa fito na fito tsakanin jami'an.


Wasu bayanai sun nuna cewa an raunata wani soja a lokacin fadar yayin da jami'an FRSC suka yi garkuwa da daya daga cikin jami'an AEPB.

Su kuma jami'an soji da yansanda suka kama jami'in FRSC guda daya suka yi garkuwa da shi.

Bayanai sun ce dukanin bangarorin guda biyu sun ja daga ta hanyar bukatar daya bangaren ya fara sako wanda ya kama.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN