Asirin Lauyan bogi ya tonu a cikin Kotu, yansanda sun yi awon gaba da shi

Wani Lauyan bogi mai suna Chris Elisha ya fada hannun yansanda, Chris ya bayyana a wani Kotun Majistare a Ojo na garin Lagos inda ya tsaya wa wani da ake tuhuma amma ya kasa gabatar da kuduri na tantance ka'iadar beli ga wanda yake karewa a Kotu.

Shi dai wannan Lauyan ya shekara 15 yana gabatar da kansa a matsayin Lauya, amma daga karshe ya gamu da kalubale daga wani Lauya mai suna Nnamdi Samuel Nwafor lamari da ya jawo hankalin yansanda da ke sintiri a Kotun.

Sakamakon haka ne yansanda suka tafi da Lauyan zuwa ofishinsu da ke Ojo inda ya shaida masu cewa ya yi karatun Lauya a Jami'ar Ukrain ta gabas a tsohuwar tarayyar Soviet amma ya kasa gabatar da takardar shaidar karatun.

Lauyan ya shaida wa yansanda cewa shi dan asalin garin Avodim Ubakala ne a jihar Abia.

Jami'an yansanda na sashen X-squad suna ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN