Wata kungiyar aikin sintiri na banga da ake kira ‘Agbor Gha Ihun’ a garin Agbor a jihar Delta sun yi nassarar damke wadansu matasa biyu bisa zargin yin sata a wani shagon wayoyin salula ranar Laraba.
Wadanda aka kama 'yan asalin jihar Plateau ne kuma suna aikin gadi ne a wasu gidaje a garin na Agbor.
Sabon chiyaman na tsaron hanyoyin ruwa da tudu na jihar Delta Mr. Monday Kiyem wanda aka fi sani da Maduma ne ya jagoranci gudanar da aikin kama matasan.