Gwamnatin Najeriya ta mayar da martani kan wasikar Obasanjo

Gwamnatin Muhammadu Buhari a Najeriya ta mayar da martani kan wasikar tsohon shugaban kasar Cif Olusegun Obasanjo wanda ya bukaci kar shugaban ya nemi tazarce a zaben 2019.
Martanin da gwamnatin ta mayar a wata sanarwar da Ministan yadda labaran kasar Lai Mohammed ya fitar, ta ce neman wa’adi na biyu ba shi ne a gaban shugaban yanzu ba.

Jami’in gwamnatin ya ce babu laifi a wasikar tsohon shugaban, kuma sun ji dadin cewar ya fahimci nasarorin da suka samu a fanin yaki da cin hanci da rashawa da fanin tsaro, wanda ke cikin abubuwa 3 na yakin neman zabensu.

Ministan ya kuma ce da alama tsohon shugaban ayyuka sun masa yawa, shiyasa bai ga kokarinsu ba a fanin farfado da tattalin arzikin kasar wanda babu shaka sun fuskanci kalubali a wannan bangare amma yanzu komai na dai-daita.

Mista Lai ya ce akwai ‘yan Najeriya da dama da ke kiraye-kirayen neman shugaba Buhari ya yi tazarce wasu kuma na adawa, sai dai kuma abin da shugaban ya sanya a gaba yanzu shi ne yadda zai shawo kan matsalolin da kasar ke ciki ba takara ba.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com *** GURBIN TALLA *** Kana son ka yi flashing ko ka cire makulli watau security na wayar ka? ka zo SENIORA TECH a OLUMBO PLAZA yamma da Gidan Wazirin Gwandu kan titin Ahmadu Bello a garin Birnin Kebbi. Shago Lamba 51 hawa na sama.

Daga rfi

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN