Gwamnatin jihar Kebbi ta ayyana Juma'a 22, Satumba ranar hutu


Gwamnatin Jihar Kebbi karkashin Jagoracin Gwamnan Jihar Sen Abubakar Atiku Bagudu ta ware gobe Juma'a  1 Al-Muharram 1439 AH Wanda ya yi daidai da 22/09/2017 a Matsayin Hutu, na Sabuwar Shekarar Musulunci.

Wannan ya biyo Bayan sanarwar da Mai Alfarma Sarkin Musulim, Sa'adu Abubakar lll ya fitar na ganin jinjirin Watan Al-Muharram 1439 yau a fadarsa da ke Sokoto.

Kuma Maigirma Gwamnan Jihar Kebbi Sen Abubakar Atiku Bagudu ya tara Sarakun Gargajiya yau a Fadar Gwamnatin Jihar, da su bada Wannan sanarwar a Masallatan Juma'a tare da yi ma kasa addu'ar zama lafiya da kuma Kara ma shugaban kasa Muhammad Buhari Kwarin guiwa wajen gudanar da Mulkin sa.


Kaunace mu a Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN