Hukumar tsaro ta farin kaya a
Najeriya ta gargadi hukumomin tsaro da na yaki da cin hanci da rashawa
da su daina amfani da sunanta wajen aiwatar da ayyukan da suka saba wa
doka a sassan kasar.
Hukumar ta ce masu yin wannan aikin na neman a yarda da aikinsu ne, tana mai bayar da misali da samamen da aka kai gidan tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Namadi Sambo, a Kaduna.
Sanarwar ta kuma ce ba ita ta kai samamen da aka kai wani ofishin kamfanin makamashi na Sahara Energy Company a Abuja ba.
Saboda haka hukumar ta ce ya kamata mutane su gane cewar ba dukkan jami'an tsaro masu sanye da bakaken kaya ne jami'ansu ba.
Hukumar ta ce tana iya kokarinta na kawo karshen wannan dabi'ar, tana mai karawa da cewar za ta ci gaba da bayyana wa masu ruwa da tsaki abubuwan da ke tafe a ayyukanta.
Ta kuma nemi mutane da ke da bayanai game ayyukan da ake zargin cewar ana yin su ba bisa ka'aida ba, da su tsegunta mata lamarin.
An dade ana sa-in-sa tsakanin hukumomin tsaro a Njeriya, amman ba safai yake fitowa fili irin wannan ba.
Ku biyo mu a
https://www.facebook.com/isyakuweb
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye.
Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120.
Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.
Daga BBC
Tags:
LABARI