Kotu ta yanke wa barawon N3.420 hukuncin kisa

Wata babban Kotu a garin Osogbo na jihar Osun ta yanke hukuncin kisa wa wani mutum mai suna Kayode Adedeji a bisa samunsa da laifi akan fashi inda ya kwace N3.420 a hannun wata mata.

Mai gabatar da kara ya shaida wa Alkalin Kotun cewa wanda ake tuhumar ya je gidan wata mata mai suna Omowunmi Adebayo a unguwar Bolorunduro Ilesa da misalin karfe 1:30 na dare rike da wuka inda ya aikata wannan fashin.

Bayanai sun nuna cewa wanda ake tuhuma ya aikata laifin ne ranar 25, ga watan Afrilu 2009,amma aka bayar da shi beli kuma daga bisani ya saba ka'idar beli inda ya sake aikata wani laifin da yasa aka sake komawa dashi Kotu.

Alkalin Kotun Justice Akano ta yanke wa Kayode Adedeji hukuncin kisa bayan Kotu ta gamsu da hujjoji akan laifi da ya aikata.



Ku biyo mu a
https://www.facebook.com/isyakuweb
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye.
Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120.
Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN