Najeriya ta baiwa mutum 335 'yan kasan waje 'yancin zama 'yan Najeriya

Gwamanatin tarayyar Najeriya ta baiwa mutum 335 takardar 'yancin zama 'yan Najeriya cikin su har da matar tsohon Gwamnan jihar Edo Lara Oshiomhole 'yar asalin kasar Cape verde.

Wannan ya biyo bayan kammala bincike da cika ka'idodi daga jami'an tsaron Najeriya wajen binciken wadanda abin ya shafa kafin a amince da zamansu 'yan Najeriya.

Ministan harkokin cikin gida Gen Abdulrahman Danbazau ya shaida wa manema labarai cewa mutum 500 ne suka mika takardar su ta neman zama 'yan Najeriya amma 335 suka cimma ka'idodin da ake bukata 245 kuma daga cikin su a bisa dalilin dadewa a Najeriya sai kuma 90 daga cikin su wanda sun zama 'yan Najeriya ne saboda sun auri 'yan Najeriya.


@isyakuweb  https://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN