Yan kasar Najeriya sun fusata matuka kan milyoyin Naira da 'yan majalisar dokokin kasarsu ke karba a matsayin albashi,a daidai lokacin da al'uma ke cikin halin kaka-ni-kayi.
A
'yan kwanakin da suka gabata, daya daga cikin sanatocin Najeriya,Shehu
Sani wanda ke wakiltar al'umar Kaduna da ke arewa masu yammacin
kasar, ya bayyana cewa 'yan majalisar dokokin kasarsa na karbar albashin
akalla dalar Amurka 35.500 (Naira milyan 13.5).
Abinda
ya bakanta wa talakawan Najeriya wadanda ke kuka babu,inda tuni
zazzafan cece-kuce suka barke a kafafan yada labarai da shafukan sada
zumunta.
Daya da cikin manyan masana a fannin tattalin arzikin Najeriya Odilim Energet ya ce :
"Bai kamata ba mu bai wa 'yan majalisar kasarmu wuka da nama wajen yanka wa kansu albashi san ranu"
Wani ma'aikacin gwamnati da ke Abuja babban birnin Tarayya,Usman Muhammad ya ce
"Babban kunya ace 'yan majalisar na karbar irin wannan albashin a daidai lokacin yawanci al'umarmu ke fama da fatara"
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
TRT
Tags:
LABARI