Daga Nura Bena, Isyaku Garba |
An yaba wa Gwamnan jihar Kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu akan irin kokari da kuma kulawar da yake bayarwa ga harkar feshin tsuntsayen Jan baki da sauran kwarin dake yiwa manoma da amfanin gona barazana, tare da barnata masu amfanin gona mai yawa.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
An yaba wa Gwamnan jihar Kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu akan irin kokari da kuma kulawar da yake bayarwa ga harkar feshin tsuntsayen Jan baki da sauran kwarin dake yiwa manoma da amfanin gona barazana, tare da barnata masu amfanin gona mai yawa.
Mataimakin Gwamnan jiha Alh. Samaila Yombe Dabai ne ya yi
wannan yobon a lokacin da ya ke amsa tambayoyin mane ma labarai a Arewa
house dake Kaduna.
Alh. Samaila Yombe Dabai ya ce dole ne a jijina wa mai girma Gwamnan jiha Sanata Atiku Abubakar Bagudu akan bada
kulawa ta musamman na yaki da tsuntsaye a cikin lokaci.
Mataimakin Gwamnan ya kara da cewa gwamnatin jihar kebbi, Gwamnatin talakawa ce domin a ko wane lokaci tana sauraren
jama'arta,tare da biyan bukatun su, hadi da kyautawa al-umma a fanni
daban - daban na rayuwa.
Ya kara da cewa, bisa ga haka ne ma, kananan hukumomin jihar ke godiya ga Gwamnatin jiha akan daukar matakan gaggawa na ceto manoman su daga barazanar tsuntsaye da sauran amfanin gona mai tarin yawa.
Ya kara da cewa, bisa ga haka ne ma, kananan hukumomin jihar ke godiya ga Gwamnatin jiha akan daukar matakan gaggawa na ceto manoman su daga barazanar tsuntsaye da sauran amfanin gona mai tarin yawa.
Alh. Samaila Yombe Dabai, ya ce Allah ya Albarkan ci jihar
kebbi da fadamar noma da sauran wuraren aikin noma mai fadi, wanda
kusan 85% na jama'ar jihar nan manoma ne , Kuma sai gashi shugaban
kasa General Muhammadu Buhari ya baiwa Gwamnan jiha shugan noman
shinkafa na kasa baki daya, da manufar bunkasa tattalin arzinkin kasa
da ma Afrika gaba daya.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com