Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Alh. Samaila Yombe Dabai ranar Laraba ya gabatar da kansa domin tantancewa a shiri da ake gudanarwa na tantance tsoffin soji a Barikin soji da ke Dukku Barracks a garin Birnin kebbi.
Yombe ya yaba wa tsarin bisa seti da aikin ke tafiya tare da nuna muhimmancin wannan aikin na tanatancewa ,ya ce sai an tantance tsoffin sojin kafin su sami kudaden su na pansho.
Haka zalika ya kara da cewa tsoffin sojin sun taka muhimmiyar rawa domin ganin Najeriya ta kasance bisa darajar ta , ya yi kira ga tsofin sojin akan su kara hakuri domin a tantance su saboda aikin na tafiya a bisa tsari.