Gwamnatin Najeriya ta ware Naira miliyan 375.8 don
biyan masu fallasa kudaden sata 20 da suka taimaka hukumomin kasar
wajan gano Naira Biliyan 11.6.
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka aiko mana rahotu ? ka tuntube mu a birninkebbi080@gmail.com
Daga RFI
A
cikin wata sanarwa da ta fitar, Ma’aikatar Kudin kasar da ta tabbatar
da sakin kudaden ta ce, a karon farko kenan da ake biyan mutane
karkashin tsarin fallasa kudaden satar.
Sai dai gwamnati ba ta bada bayani ba game da mutanen da suka amfana da kudaden saboda dalilai na tsaro.
Ma’aikatar Kudin ta ce, matakin biyan ya nuna irin yadda gwamnatin Muhammadu Buhari ta mayar da hankali don cika alkawarinta ga masu fallasar, wadda ke da muhimmanci wajen yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya.
Gwamnati na bai wa masu fallasar akalla kashi 5 cikin 100 na kudaden da suka bayar da bayanansu kuma aka gano su, amma an tanadi hukuncin dauri a gidan yari kan duk wanda ya fallasa bayanan karya.
Sai dai gwamnati ba ta bada bayani ba game da mutanen da suka amfana da kudaden saboda dalilai na tsaro.
Ma’aikatar Kudin ta ce, matakin biyan ya nuna irin yadda gwamnatin Muhammadu Buhari ta mayar da hankali don cika alkawarinta ga masu fallasar, wadda ke da muhimmanci wajen yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya.
Gwamnati na bai wa masu fallasar akalla kashi 5 cikin 100 na kudaden da suka bayar da bayanansu kuma aka gano su, amma an tanadi hukuncin dauri a gidan yari kan duk wanda ya fallasa bayanan karya.
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka aiko mana rahotu ? ka tuntube mu a birninkebbi080@gmail.com
Daga RFI
Tags:
LABARI