Zanga-zanga ta sake barkewa a wata jihar Najeriya kan matsin tattalin arziki


Matasa a jihar Osun a ranar Juma’a, 9 ga watan Fabrairu, sun gudanar da zanga-zangar lumana a Osogbo, babban birnin jihar, kan matsalar tattalin arziki da ake ciki a fadin kasar nan.


 Zanga-zangar wacce aka yi wa lakabi da ‘Osun Peaceful Solidarity Walk’, ta gudana ne a gefen dajin Freedom da ke Osogbo.  Masu zanga-zangar sun ce tsadar rayuwa ta zama abin da talaka ba zai iya jurewa ba.


 Da yake zantawa da manema labarai, wanda ya shirya zanga-zangar, Kwamared Owolabi Hassan Oluwatobi, ya ce ‘yan Najeriya na cikin mawuyacin hali sakamakon matsin tattalin arzikin da kasar ke ciki.


 Shugaban gamayyar kungiyoyin farar hula a jihar, Kwamared Waheed Lawal ya yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya gaggauta magance matsalar tattalin arzikin kasar nan.


 Lawal ya ce kungiyar farar hula a jihar za ta shirya gagarumin zanga-zanga matukar gwamnatin tarayya ta gaza samar da mafita ga matsalar tattalin arziki.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN