Rundunar yan sandan jihar Bauchi ta ayyana neman Dokta Idris Abdulazeez Dutsen Tanshi ruwa a jallo


Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta ayyana neman wani malamin addinin Islama a Bauchi, Dokta Idris Abdulazeez Dutsen Tanshi, ruwa a jallo bisa zarginsa da cin zarafin kotu.


 Rundunar ta bayyana hakan ne a cikin wata takarda ta ‘yan sanda ta musamman da aka fitar a ranar Alhamis, 8 ga Fabrairu, 2024.


 “Idan an gan shi, a kama shi a mikawa ofishin ‘yan sanda mafi kusa ko ofishin mataimakin kwamishinan ‘yan sanda, sashin binciken manyan laifuka na jihar Bauchi, ko a kira lambar waya 08151849417, 09048226246,” ya kara da cewa, “Kyakkyawan tukuicin yana jiran kowane mutum da ya bayar da bayanin da ya kai ga kama shi," in ji shi.


 Tun a shekarar 2022 ake shari'ar Sheikh Idris wanda ke fuskantar shari'a bisa zarginsa da kalaman batanci ga addini.


 Sauran tuhume-tuhumen da malamin ke fuskanta kamar yadda babban mai shari’a kuma kwamishinan shari’a a jihar da ‘yan sanda suka shigar a babban kotun majistare sun hada da tada hankulan jama’a, cin zarafi ko kuma tada jijiyar wuya na addini.


 Idris, a daya daga cikin wa’azin da ya yi, ya yi nuni da cewa zai tafi gudun hijira sakamakon barazanar da ya yi zargin Yana fuskanta daga gwamnan jihar, Bala Mohammed.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN