Yan sanda sun kama mai garkuwa da mutane da ya kashe Nabeeha


Rundunar ‘yan sandan Najeriya, a ranar 20 ga watan Janairu, 2024, sun kama wani kasurgumin mai garkuwa da mutane mai suna Bello Mohammed, mai shekaru 28, wanda ake zargin ya kashe Nabeeha, budurwar da aka sace tare da wasu ‘yan uwanta mata guda biyar a Bwari, Abuja a ranar 2 ga watan Janairu, daga baya aka kashe ta bayan danginta sun kasa bayar da kudin fansa da aka nema.



 Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Najeriya Muyiwa Adejobi ya fitar, ta ce jami’in ‘yan sandan shiyya ta Tafa a lokacin da take aikin leken asiri ta kai samame wani otal da ke Unguwar Tafa a Kaduna, inda ta kama Bello da kudi naira miliyan 2.25.  (Miliyan biyu, da naira dubu dari biyu da hamsin) kacal, wadanda ake zargin kudin fansa ne da aka karba daga wadanda aka sace a yankin.



 Adejobi ya bayyana cewa wanda ake zargin, yayin da ake masa tambayoyi, ya amsa cewa yana cikin kungiyar da ta yi garkuwa da dangin wani Barista Ariyo a Bwari,FCT, a ranar 2 ga watan Janairu, 2024, tare da kashe wasu da aka yi garkuwa da su, ciki har da Nabeeha, diyar wata mata da Lauya, ranar 13 ga Janairu, 2024, a sansanin masu garkuwa da mutane, a jihar Kaduna.



 Ya ce wanda ake zargin a cikin wani yanayi mai ban mamaki, ya bayar da #1,000,000 (Naira miliyan daya kacal) domin ya jawo DPO na yankin Tafa SP Idris Ibrahim, wanda ya ki amincewa da wannan tayin, ya kuma gudanar da aikinsa da gaske ya damke Bello kasurgumin mai garkuwa da mutane.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN