Shekarar 2023 ta zo mana da manyan kalubale, Abba Kabir, Kwankwaso sun magantu kan shekarar 2024


Gwamna Abba Kabir da mai gidansa Rabiu Kwankwaso sun yi martani kan shiga sabuwar shekarar 2024.

 Wanna na kunshe ne a cikin sanarwa da suka wallafa a shafukansu na X a yau Litinin 1 ga watan Janairu.  Legit Hausa ya wallafa.

A martaninshi, Gwamna Abba Kabir ya taya dukkan jama’ar jihar Kano murnar shiga sabuwar shekarar lafiya.

Abba ya ce ya na da tabbacin cewa sabuwar shekarar da za a shiga za ta zamo shekarar samun ci gaba ga jihar Kano.

Ya ce gwamnatinsa ta himmatu wurin tabbatr da bukatun al’umma sun samu kulawa don samar da ci gaba a jihar. 

Ya ce: “Ina taya al’ummar jihar Kano murnar wannan rana, ina da tabbacin sabuwar shekarar za ta kawo ci gaban da ba a taba gani ba ga al’ummar jihar. 

Gwamnatina za ta ci gaba da kula da bukatun al’umma don samar da ci gaba a bangarori da dama a jihar.” 

Ya ce tabbas an samu matsaloli da dama a shekarar da ta gabata inda ya ce sabuwar shekarar za ta zo da ci gaba. 

Ya ce: “Ina cikin farin ciki da tura gaisuwa ga ‘yan Najeriya gida da waje kan murnar shiga sabuwar shekara. 

“Tabbas shekarar da ta wuce an samu matsaloli a kasar baki daya, kuma ina fatan sabuwar shekarar za ta zo da zaman lafiya da kwanciyar hankali.” 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN