An kuma: Wani dan kasuwa ya rataye kansa har lahira saboda bashi


Wani dan kasuwa mai suna D1 ya kashe kansa saboda bashi a jihar Ogun.


 Lamarin ya faru ne a unguwar Idi Orogbo da ke Araromi a cikin Sango-Ota a ranar Talata, 30 ga Janairu, 2024.


 Wasu majiyoyi na kusa da marigayin sun shaida wa jaridar Nigerian Tribune cewa an gano gawar D1 a rataye a jikin wani gado a daya daga cikin shagunan sa guda biyu da ya kwana.


 Majiyar ta ce matakin da D1 ya yanke na kawo karshen rayuwarsa watakila ba zai rasa nasaba da bashin da ya ci ba.


 An kuma tattaro cewa marigayin na shirin rasa gidansa ne sakamakon bashin da ake binsa.


 "Matar sa ce ta gano D1 a rataye a saman rufin, wacce ta zo duba shi," in ji majiyar.


 “Tun wani lokaci yanzu yana fama da matsalar kudi sosai, yana da shaguna guda biyu inda yake siyar da CD na bidiyo.


 Wani Mazauni garin ya ce an kai rahoton lamarin a ofishin ‘yan sanda reshen Sango Ota.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN