Jerin mutane 8 da suka bada taimakon miliyan 700 da aka kashe masu Maulidi a Tudun Biri a Kaduna


Ana tsakiyar taron maulidi sojoji su ka harba bam-bamai, suka kashe mutane a Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna. Legit Hausa ya wallafa.

Su wanene suka bada gudumuwa a Tudun Biri?

1. Sanatocin Najeriya (N109m)

Duk Sanatocin kasar nan 109 sun yi abin a-yaba da su ka ware albashinsu domin a taimakawa mutanen da wannan hari ya shafa.

An rahoto cewa ‘yan majalisar dattawan za su hada N109m domin al’ummar Tudun Biri.


2. ‘Yan majalisar wakilai (N350m)

Alhassan Ado Doguwa ya sanar da cewa ‘yan majalisar tarayya za su bada gudumuwar N350m bayan kashe mutane kusan 100 da aka yi.

Hon. Ado Doguwa ya shaida haka lokacin da su ka ziyarci garin Kaduna 


3. Shugaban majalisar wakilai (N45m)

A matsayinsa na shugaban majalisa da kuma sauran abokan aikinsa daga Kaduna, Rt. Hon. Tajuddeen Abbas sun yi alkawarin bada N45m.

4. Khalifa Muhammadu Sanusi II (N10m)

Ana rade-radin cewa Muhammadu Sanusi II ya ba mutanen wannan gari tallafin N10m a matsayinsa na Khalifan darikar Tijjaniya a Najeriya.

5. Nasir El-Rufai (N10m)

A rahoton da ba a tabbatar ba, an ce Nasir El-Rufai wanda ya ziyarci garin tare da Muhammadu Sanusi II shi ma ya bada gudumuwar N10m.

6. Peter Obi (N5m)

‘Dan takaran shugaban kasa a karkashin jam’iyyar LP, Peter Obi ya ziyarci garin Tudun Biri domin yi masu ta’aziyyar rashin da su ka yi.

Peter Obi ya je asibitin Barau Dikko kuma ya bada gudumuwar N5m ga wadanda ke jinya kamar yadda Vanguard ta fitar da rahoto a baya.

7. Gwamnonin Arewa (N180m)

Bayan harin sojojin, Gwamnan Kwara ya ziyarci Kaduna a matsayin shugaban gwamnonin Arewa. Wata majiya ta ce ya bada kudi.

A taron gwamnonin Arewa, an tabbatar da cewa NGF ta bada gudumuwar N180m.

8. Jam’iyyatu

 Ansariddeen Attijjaniyya (N3.9m)
People Gazette ta ce kungiyar darika ta Jam’iyyatu Ansariddeen (Attijjaniyya) ta raba gudumuwar kayan wanki da tufafi N3.9m a Tudun Biri.

'Yan Tudun Biri sun kai gwamnati kotu?
Mukhtar Usman ya je kotu kamar yadda aka ji, ya ce Naira biliyan 33 al'ummar Tudun Biri su ke nema daga aljihun gwamnati a matsayin diyya.

Daga baya mutanen sun ce ba su shigar da kara a kotun tarayya mai zama a Kaduna.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN