Dan Najeriya ya nemo aikin da ake biyan albashi miliyan 2.6 duk wata a Lagas, WAEC kawai ake bukata


Wani matashi dan Najeriya ya yiwa jama'a tayin aiki mai tsoka a ofishin jakadancin Amurka da ke Lagas, Najeriya, wanda ke nuni da cewar akwai gurbin aiki na wanda zai taimaka da aikace-aikace a ma'aikatar

Wanda ya yi nasarar samun aikin zai kasance yana gudanar da ayyukansa a karkashin sashen ba da shawarwari na ma'aikatar. Legit Hausa ya wallafa.

Ayyukan da zai rinka yi sun hada da tsara ganawar jama'a da sashen ma'aikatar, samar da takardar biza ga jama'a da kuma adana bayanan duk ayyukan da ya ke yi a cikin kundin ajiyar ma'aikatar.

Albashin wannan mukamin shine ₦2,699,000 duk wata, wanda ya yi daidai da kimanin $2,500. Abun da ake bukata shine takardar shaidar kammala karatun sakandare (SSCE), amma za a fi son wadanda suka mallaki kwalayen OND, HND, ko digiri.

Za a rufe neman aikin wannan mukami a ranar 1 ga watan Fabrairun 2024.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN