Wasu fusatattun hafsoshin sojin saman Najeriya sun bayyana takaicinsu kan harin da sojojin Najeriya suka kai a Tundun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna.
Sama da rayuka 120 ne aka ruwaito sun mutu, sama da 60 kuma suka jikkata bayan da wani jirgin yaki mara matuki na soja ya kai harin bama-bamai a kauyukan da suke bikin Maulud a daren Lahadi. Daily trust ta wallafa.
Jami'an NAF sun ci gaba da cewa su (sojoji na sama) suna da isasshen horo da kayan aiki don gudanar da ayyukan jiragen sama "tare da daidaito" fiye da sauran ayyuka na soja.
“Kowace ma’aikata ko hukumar tsaro tana da rawar da ta taka duk da cewa dukkanmu mun yi horo iri daya. Maganar gaskiya ita ce, sojojin sama sun fi sauran sojoji masana da jiragen sama marasa matuka ko kuma a kai farmaki,” kamar yadda daya daga cikin jami’an NAF ya shaida wa Daily trust.
Sai dai wasu hafsoshin sojojin sun yi iƙirarin cewa, babu wani babban al'amari wajen sarrafa jiragen matasa matuka da za su yi yaƙi da abokan gaba, inda suka ƙara da cewa wannan ba shi ne karon farko da suka yi amfani da su ba.
"Gaskiyar cewa mun yi kuskure a wannan karon ba yana nufin ba za mu iya tashi da jirgi mara matuki a kan abokan gaba ba. Muna da iyawa kuma muna da damar tashi da shi, ”in ji jami’in sojan.
Sai dai wata majiya da ke magana da jami’ai a runduna da sojojin sama ta ce za a iya kaucewa abin da ya faru a Tudun Biri.
“Kafin su jefa bam a kan masu bikin Mauludi, a zahiri wasu jami’an sojojin sun yi ta ishara da wasu jami’an sojin sama, kuma an yi musu gargadin cewa taron ba na ‘yan ta’adda ba ne.
"Sun gaya musu (sojoji) cewa 'yan ta'adda ba sa haduwa da yawa a cikin al'umma. Haka nan duk inda ka ga ‘yan ta’adda ko ‘yan fashi suna haduwa, za ka ga babura da yawa. Babu babura a wurin Mauludin a ranar…A gaskiya abin takaici ne,” inji majiyar.
From ISYAKU.COM