An bai wa hammata iska tsakanin jami'an DSS da na NSCDC, da dama sun samu raunuka


An samu hargitsi tsakanin jami’an hukumar DSS da kuma jami’an hukumar NSCDC a jihar Edo. 

Lamarin ya faru ne a yau Litinin 4 ga watan Disamba a cikin asibitin kwararru da ke birnin Benin City a jihar, Legit ta tattaro. 

Hargitsin ya fara ne yayin da jami’an DSS su ka kawo dan uwansu zuwa asibitin bayan ya fadi yayin wani taro wanda ma’akatan asibitin ba su musu tarba mai kyau ba. 

The Nation ta tattaro cewa an samu daidaito bayan shiga lamarin da shugaban masu tsaron gidan gwamnati ya yi da kuma hukumar ‘yan sanda. 

Wani daga cikin jami’an DSS ya bayyana yadda abin ya faru inda ya ce ba su samu tarba mai kyau a asibitin ba inda su ke bukatar kulawar gaggawa. 

Daraktan asibitin, Dakta David Odiko ya ce jami’an DSS sun ki amincewa sun kawo shi matacce amma likita ya kula da shi har ya fada musu cewa ya mutu. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN