Soji sun harbe wanda ake zargi da sace akwatin zabe a garin Anyigba na jihar Kogi


Jami’an soji sun kashe wani mutum da aka ce yana goyon bayan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki a jihar Kogi, Umoru Agabidu.


 An bayyana cewa wanda ake zargin ya je rumfar zabe da ke Agala Ogane, Anyigba a karamar hukumar Dekina a jihar, domin kwace akwatin zabe yayin da ake ci gaba da kada kuri’a.


 An yi zargin cewa jami’an soji da ke bakin aiki a sashin zabe ne suka harbe Umoru da misalin karfe 10:00 na safe.


 A cewar wani shaidan gani da ido, Umoru ya damke na’urar BVAS da karfin tsiya sannan ya farfasa ta a kasa a kokarinsa na daina kada kuri’a a rumfar zabe.


 Wata majiya ta ruwaito cewa, “Wannan ya faru ne a sashin zabe da nuke zaune.  Sun gargade shi da kada ya dauki akwatin zabe amma bai saurare su ba.  Sojoji ne suka harbe shi a lokacin da yake shirin tafiya da akwatin zabe.”


 Masu makoki sun yada hotunan Umoru domin makokinsa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN