Da duminsa: Saudiyya ta soke biza dukkan fasinjoji 264 da suka yi tafiya daga Najeriya zuwa Jeddah


An shiga dimuwa da mamaki yayin da Hukumomin Saudiyya suka soke bizar dukkan fasinjoji 264 da aka dako daga Kano da Legas a ranar Lahadi.


Jami'an na Saudiyya sun dage cewa jirgin ya mayar da su Najeriya inda ya dako su. Legit Hausa ya wallafa.


Jirgin ya tashi ne daga filin jirage na Murtala Mohammed, Legas ta filin Malam Aminu Kano da ke Kano a daren ranar Lahadi ya kuma dira filin Sarki Abdul-Aziz, Jeddah a Saudiyya, rahoton Daily Trust.


Amma abin mamaki ga ma'aikatan jirgin, Hukumomin Saudiyya suka sanar cewa an soke bizar dukkan fasinjojin.


Hakan na zuwa ne duk da cewa dukkan fasinjojin an musu bincike na APIS a Najeriya kafin su taso kuma jami'an Saudiyya suna sa ido a kai.




Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN