Matar mai suna Hope Nwala ana zargin ta da watsawa mijinta, Ekelediri Nwanko man gyada kan wata karamar jayayya, cewar Punch.
Nwala ta aikata laifin ne a kauyen Okehi da ke karamar hukumar Etche a jihar bayan mijin ya kwanta bacci. Legit Hausa ya wallafa.
Kakakin rundunar 'yan sanda a jihar, Grace Iringe-Koko ta tabbatar da faruwar lamarin inda ta ce matar na hannun jami'ansu, Newstral ta tattaro.
Grace ta ce jami'ansu sun yi nasarar kama matar ce bayan ta tsere ganin girman laifin da ta aikata.
Ta ce:
"An kama matar kuma ta na hannun jami'anmu, an cafke ta ne a yau Alhamis 12 ga watan Oktoba.
"A yanzu haka ana kan bincike wanda da zarar an kammala za a dauki matakin da ya dace."
DAGA ISYAKU.COM