An yi wa wata mata bulala a bainar jama'a bisa zarginta da satar daurin plantain guda uku a jihar kudu


Wasu shugabannin matasa sun yi wa wata mata mai suna Obot Udo Ekpo bulala bisa zarginta da satar wasu hannun plantain guda uku a kauyen Okon Eket da ke jihar Akwa Ibom. Shafin isyaku.com ya samo.


 An tattaro cewa an kama wanda ake zargin ne a safiyar Litinin, 16 ga Oktoba, 2023.


 Rahotanni sun bayyana cewa ta so ta sayar da plantain da ta sace a babbar kasuwar Urua Udo Inyang da ake ci a mako-mako, wanda a yau ne, amma sai aka kamata dumu-dumu.


 Wanda ake zargin wanda ta fito daga Ikot Akpandem a Okon Eket, shugaban matasan kauyen, Akparawa Uyai Udo Jacob, ya mika ta ga ‘yan sanda da ke yankin Uqua domin bincike da gurfanar da ita gaban kuliya.

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN