An yi wa wata mata bulala a bainar jama'a bisa zarginta da satar daurin plantain guda uku a jihar kudu


Wasu shugabannin matasa sun yi wa wata mata mai suna Obot Udo Ekpo bulala bisa zarginta da satar wasu hannun plantain guda uku a kauyen Okon Eket da ke jihar Akwa Ibom. Shafin isyaku.com ya samo.


 An tattaro cewa an kama wanda ake zargin ne a safiyar Litinin, 16 ga Oktoba, 2023.


 Rahotanni sun bayyana cewa ta so ta sayar da plantain da ta sace a babbar kasuwar Urua Udo Inyang da ake ci a mako-mako, wanda a yau ne, amma sai aka kamata dumu-dumu.


 Wanda ake zargin wanda ta fito daga Ikot Akpandem a Okon Eket, shugaban matasan kauyen, Akparawa Uyai Udo Jacob, ya mika ta ga ‘yan sanda da ke yankin Uqua domin bincike da gurfanar da ita gaban kuliya.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN