Yan bindiga sun kashe mutane 2 sun sace mutane 7 a jihar Kebbi


Wasu ‘yan bindiga da suka kai farmaki kauyen Kwarikwarasa da ke karamar hukumar Maiyama a jihar Kebbi a karshen makon da ya gabata, sun kashe mutane biyu tare da yin garkuwa da wasu mutanen kauyen su bakwai.

 Daily trust ta ruwaito cewa yan bindigan sun mamaye al’ummar ne da sanyin safiyar ranar Asabar, 9 ga watan Satumba.

 Gwamna Nasiru Idris ya ziyarci al’umma inda ya tabbatar da cewa gwamnati ta tanadi matakan dakile sake afkuwar lamarin.  Ya ce ya bai wa jami’an tsaro dukkan goyon baya da hadin kan da ya kamata domin yakar miyagun ayyuka a fadin jihar.


Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN