Yan bindiga sun dira gidan Dansanda sun sace diyarshi mai shekara 11 suka halaka ta a dajin Zamfara


Wasu ‘yan bindiga dauke da makamai sun kashe diyar wani dan sanda mai shekaru goma sha daya a Gusau babban birnin jihar Zamfara.


 An kashe yarinyar mai suna Hauwa’u Lawali, bayan an sace ta daga gidan mahaifinta da ke unguwar Saminaka a Gusau.


 An tattaro cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki gidan dan sandan da ke aiki da rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara a daren ranar Lahadi, 3 ga watan Satumba, 2023, inda suka yi awon gaba da yarinyar.


 A cewar wani rahoton gidan talabijin na TVC, masu garkuwa da mutanen sun harbe yarinyar ne a ranar Litinin din da ta gabata, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa daji bayan da suka lura cewa jami'an tsaro na bin su.


 Hukumomin ‘yan sanda a Zamfara sun tabbatar da faruwar lamarin, inda suka ce har yanzu jami'an tsaro suna cikin daji suna bin ‘yan ta’addan.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN