Kotun kararrakin zabe ta tabbatar wa Gwamnan APC a Sokoto kujerarsa, ta yi watsi da korafin dan takarar PDP


Kotun sauraren kararrakin zaben gwamnan jihar Sokoto ta yi watsi da karar da Sa’idu Umar dan takarar jam’iyyar PDP ya shigar yana kalubalantar nasarar Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan Sokoto a zaben ranar 18 ga watan Maris.

 Sa’idu Umar ya tunkari kotun don yin watsi da nasarar Aliyu. The Nation ta rahoto.

 Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayyana Aliyu a matsayin wanda ya lashe zaben, amma Umar ya fafata da Aliyu inda ya ce mataimakin Aliyu Idris Gobir bai cancanta ba, kuma an tafka magudi a zaben.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN