Mutuwar Yan Mata 8 a hadarin kwalekwale: Gwamnan jihar Kebbi ya yi Ta'aziyya da jaje ga muanen kauyen Kurya



Gwamnan jihar Kebbi ya jajenta tare da Ta'aziyya ga al'ummar garin Kurya sakamakon rasuwar yan mata takwas a hadarin kwalekwale.

Mai ba wa Gwamnan jihar Kebbi shawara kan harkokin siyasa Alhaji Kabiru Sani (Giant) ya wakilci Gwamnan jihar Kebbi Dr. Nasir Idris a wajen ta'aziyyar.

Alhaji Kabiru ya roki Allah ya jikan mamatan ya yi masu rahama.

Ya kuma mika sakon kyautar Gwamna na Naira miliyan daya (N1m) ga iyalan mamatan.

Hakimin kauyen Kurya Alhaji Aliyu Musa ya gode wa gwamna Nasir bisa wannan ziyarar Ta'aziyya da kuma kyautar da aka yi wa iyalan mamatan. Ya kuma yaba wa Gwamna bisa yadda ya sa taimakon talaka gaba, duba da yadda ya raba wa jama'a taki kyauta kuma a daidai lokaci da ake bukata.

Tawagar ta kunshi  Hon Umaru Sallah Sambawa, Dan Majalisar dokokin jihar Kebbi mai wakiltar Maiyama , Hon. Bello Abdullahi Mungadi, Alhaji Saidu Giwatazo, shugaba jam'iyar APC karamar hukumar Maiyama da sauran fitattun mutane da manyan yan siyasa.







Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN