Cire tallafi: Fusatattun talakawa sun fasa Ma'ajiyar abinci na Gwamnati sun yi wasoson abinci a Najeriya


Talakawa da aka ce sun fusata saboda wahalhalun da kasar ke fuskanta sakamakon cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi sun fasa Ma'ajiyar abinci na Gwamnatin jihar Bayelsa da ke kan titin Isaac Boro Express suka yi awon gaba da kayan abinci da ke ciki.

 Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Bayelsa (BYSEMA) ta ce kayayyakin abincin da aka kwashe ba su da amfani ga dan Adam domin an ajiye su ne a lokacin ambaliyar ruwa ta shekarar 2022 a jihar.

 Gwamnatin tarayya ta sanar da ware Naira biliyan 5 a matsayin tallafi ga jihohi domin rabawa ‘yan Najeriya.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN