Yanzu yanzu: Gwamnan Kebbi ya kori S.A saboda rashin da'a da ya wallafa a shafukan sada zumunta

Sanarwar manema labarai


Mai girma gwamnan jihar Kebbi, Dr Nasiru Idris, Kauran Gwandu, ya sauke mai ba shi shawara na musamman kan harkokin matasa daga mukaminsa.

Korar S.A. ya biyo bayan wani posting na rashin mutunci da yayi akan matsayin sa na WhatsApp (Status)

Gwamnan wanda ya fusata da wannan mumunan lamari, ya ce Mataimakin ya tattake kyawawan dabi’u da zamantakewar al’ummar Kebbi, wanda galibinsu mabiya addinin Musulunci ne.

Kauran Gwandu ya sha alwashin cewa gwamnatin sa ba za ta lamunci duk wani abu da zai zubar da mutuncin al’ummar jihar ba.

Gwamnan ya kuma gargadi sauran jami’an gwamnati da su guji yin irin wadannan munanan rubuce-rubuce a shafukansu na sada zumunta da sauran wuraren dandalin jama’a.

Sa hannu,

Ahmad Idris

Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna

10/07/2023

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN