Yadda gobara ta kama bukka da almajirai ke barci cikin dare uku suka mutu a jihar arewa


Daliban addinin Musulunci guda uku sun kone kurmus bayan da wata bukka ta kone kurmus a garin Yola na jihar Adamawa.

 Almajiran da suka rasu, suna zaune ne a harabar makarantarsu da ke Sabon Pegi a karamar hukumar Yola ta Kudu.

 An tattaro a ranar Litinin cewa biyu daga cikin daliban sun mutu nan take a lokacin da gobarar ta tashi a daren Juma’a yayin da na ukun ya rasu da safiyar Asabar a asibitin koyarwa na jami’ar Modibbo Adama da ke Yola.

 Malam Abubakar Usman wanda ya mallaki makarantar da mamacin ke karatu, ya tabbatar da cewa daliban sun rasu ne sakamakon gobarar maganin sauro.

 Ya ce biyu daga cikin daliban, Ismaila Muhammadu mai shekaru 12 da Yusuf Abubakar mai shekaru 13, sun mutu nan take yayin da Mustapha Ahmadu mai shekaru 17 ya rasu a safiyar ranar Asabar a asibiti.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN