A cewar kafafen yada labaran kasar, lamarin ya faru ne a karshen makon da ya gabata a yankin Mbagassina da ke yankin Mbam da Kim na yankin tsakiyar kasar Kamaru,
An tattaro cewa ‘yan uwan biyu sun gwabza kazamin fada a kan yarinyar mai shekaru 13 da haihuwa.
“Daya daga cikin ‘yan’uwan (Marigayin) ya ce yarinyar budurwarsa ce. Ya dade yana zargin dan uwansa yana da wata alaka da budurwarsa saboda kusancinsu,” crwar wani ganau mai suna Gildas, ya shaida wa wani dan jarida a ranar Alhamis, 6 ga watan Yuli.
“Kafin a fara faÉ—an, É—aya daga cikin ’yan’uwan ya nemi yarinyar bai gan ta ba sai ya wuce ta hanya ya sadu da ita da É—an’uwansa a zaune. Don haka sai ya tambayi yarinyar abin da take yi a wurin, sai É—an’uwansa ya yi Æ™oÆ™ari ya shiga tsakani ya kare yarinyar."
Gildas ya kara da cewa "Yanzu ya fusata, ya je gidansu, ya damko adda, ya afka wa dan'uwansa. Dan'uwan shi kuma ya ruga gida ya dauko wuka ya rama farmaki kan dan'uwansa. Haka ya sa ya mutu," in ji Gildas.
Published by isyaku.com