Matasan gari sun tafka satan buhuhuwan shinkafa, masara, a gidan ajiye kayan abinci na dan majalisa


Wasu mutane da dama sun tafka sata a wani rumbun ajiyar da aka yi amfani da shi wajen adana buhunan masara da shinkafa da aka sarrafa a cikin gida da dai sauransu a wani dakin ajiyar kaya da ke Jalingo babban birnin jihar Taraba.


 Mutanen sun mamaye rumbun ajiyar da ba ta da nisa da 6 Army Brigade, kuma na wani dan majalisar jiha ne kuma tsohon shugaban karamar hukumar Sardauna a daren Juma’a.


 Jami’an tsaro da suka isa wurin domin tarwatsa mutanen sun kashe biyu daga cikinsu.  Daily trust ta ruwaito cewa kayayyakin da aka kwashe sun hada da daruruwan buhunan masara da shinkafa da aka sarrafa a cikin gida da kuma kayayyakin amfanin gona da suka hada da taki da magungunan kashe kwari.


 Hakazalika matasan sun tafka sata a wasu shaguna a yankin. A baya ma, an kai harin sata a gidan ajiyar kayan ajiya a lokacin tarzomar EndSARS na 2020 kuma an yi awon gaba da kayayyaki na miliyoyin naira.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN