Hoto: Shugaba Tinubu ya yi taron farko da sabbin shugabannin rundunonin tsaro


A ranar Litinin ne shugaban kasa Bola Tinubu ya yi ganawarsa ta farko da sabbin shugabannin ma’aikatun tsaro da aka nada kwanan nan.

 An gudanar da taron ne a fadar gwamnatin taraya dake Abuja. Jaridar PM News ta rahoto.

Babban mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Mallam Nuhu Ribadu ne ya jagoranci shugabannin hukumomin zuwa dakin taron.

 A wajen taron akwai Manjo Janar Christopher G Musa, babban hafsan hafsoshin tsaro;

 

Manjo Janar, A Lagbaja, babban hafsan sojin kasa;  Rear Admiral Emmanuel A Ogalla, babban hafsan sojin ruwa;  Air Vice Marshal Hassan B. Abubakar, Hafsan Hafsoshin Sojan Sama;  Mukaddashin Sufeto Janar na ‘yan sanda Kayode Egbetokun da Manjo Janar Emmanuel P.A.  Undiandeye, shugaban hukumar leken asiri na tsaro.

Tinubu dai ya tafi kasar Faransa ne a daidai lokacin da ya nada sabbin shugabannin ma’aikatun kuma ya dawo Abuja ranar Lahadi.

 A ranar 19 ga watan Yuni, 2023 shugaban ya kori tsoffin hafsoshin tsaro tare da nada sababbi.

Published by isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN