Hoto: Shugaba Tinubu ya yi taron farko da sabbin shugabannin rundunonin tsaro


A ranar Litinin ne shugaban kasa Bola Tinubu ya yi ganawarsa ta farko da sabbin shugabannin ma’aikatun tsaro da aka nada kwanan nan.

 An gudanar da taron ne a fadar gwamnatin taraya dake Abuja. Jaridar PM News ta rahoto.

Babban mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Mallam Nuhu Ribadu ne ya jagoranci shugabannin hukumomin zuwa dakin taron.

 A wajen taron akwai Manjo Janar Christopher G Musa, babban hafsan hafsoshin tsaro;

 

Manjo Janar, A Lagbaja, babban hafsan sojin kasa;  Rear Admiral Emmanuel A Ogalla, babban hafsan sojin ruwa;  Air Vice Marshal Hassan B. Abubakar, Hafsan Hafsoshin Sojan Sama;  Mukaddashin Sufeto Janar na ‘yan sanda Kayode Egbetokun da Manjo Janar Emmanuel P.A.  Undiandeye, shugaban hukumar leken asiri na tsaro.

Tinubu dai ya tafi kasar Faransa ne a daidai lokacin da ya nada sabbin shugabannin ma’aikatun kuma ya dawo Abuja ranar Lahadi.

 A ranar 19 ga watan Yuni, 2023 shugaban ya kori tsoffin hafsoshin tsaro tare da nada sababbi.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN