GWAMNATIN KEBBI TA AYYANA LARABA, 19 GA JULY, 2023 HUTU DOMIN SABUWAR SHEKARAR MUSULUNCI


Gwamnan jihar, Dr. Nasir Idris, (Kauran Gwandu) ya ayyana ranar Laraba 19 ga watan Yuli, 2023 a matsayin ranar hutu domin murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci, Muharram 1445H.

 Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban ma’aikatan jihar, Alhaji Safiyanu Garba Bena wanda aka rabawa manema labarai ranar Talata a Birnin kebbi.

 Sanarwar ta ce, hakan ya biyo bayan ayyana ranar Laraba 19 ga watan Yuli a matsayin 1 ga watan Muharram, wata na farko na sabuwar shekara ta Musulunci ne domin baiwa al'ummar Musulmi damar gudanar da bukukuwan sabuwar shekarar Musulunci.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN