Da dumi-dumi: Tashin hankula bayan wata Katanga ta rufto kan wasu Yara, an samu asarar rai


Wasu ƙananan yara guda biyu, Gbolahan da Olayinka Atolagbe, sun riga mu gidan gaskiya bayan katangar wani gida dake maƙwabtaka da na su ta rufto musu a jihar Legas. Legit ya wallafa.

Jaridar The Punch ta rahoto cewa lamarin ya auku ne a lokacin wani ruwan sama mai kama da bakin ƙwarya da aka tafka ranar Asabar, a titin Alao, cikin Isawo a ƙaramar hukumar Ikorodu ta jihar.

An ciro gawarwakin yaran a cikin ɓuraguzan katangar bayan sun kwashe sa'o'i masu yawa yayin da ake ta ƙoƙarin ceto su.

Kakakin hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) yankin Kudu maso Yamma, Mr Ibrahim Farinloye, ya tabbatar da aukuwar lamarin a cikin wata sanarwa.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN