Yanzu yanzu: Tinubu ya nada shugaban ma’aikata, ya zabi Ministan Buhari a matsayin SGF


Shugaban kasa, Bola Tinubu ya nada Sanata George Akume, tsohon ministan ayyuka na musamman a matsayin sakataren gwamnatin tarayya.

 Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Daraktan yada labarai na fadar gwamnatin jihar Abiodun Oladunjoye ya fitar ranar Juma’a. Daily trust ta rahoto.

 “Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ranar Juma’a a Abuja ya sanar da nadin kakakin majalisar wakilai, Rt.  Hon.  Femi Gbajabiamila a matsayin shugaban ma’aikata, da Sen. Ibrahim Hassan Hadejia, tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa a matsayin mataimakin shugaban ma’aikata.

 “A ganawar da shugaban ya yi da Progressive Governors Forum (PGF), shugaban ya kuma nada tsohon gwamnan jihar Benue kuma tsohon ministan ayyuka na musamman, George Akume, sakataren gwamnatin tarayya (SGF).”

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN