Yanzu-Yanzu: Shugaba Tinubu Ya Bayyana Lokacin da Za'a Fara Bai Wa Ɗaliban Najeriya Bashin Kuɗi

Shugaba Bola Ahmed Tinubu

Gwamnatin tarayya karkashin jagoranci shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ta ce tana aiki ba dare ba rana domin ganin an fara bai wa ɗaliban Najeriya bashin kuɗi a watan Satumba da Oktoba, 2023.

Babban Sakataren ma'aikatar ilimi, David Adejo, ne ya sanar da haka ranar Laraba yayin da yake amsa tambayoyin 'yan jarida a birnin tarayya Abuja. Legit ya wallafa.

Idan baku manta ba, shugaba Tinubu ya rattaɓa hannu kan kudirin bai wa ɗaliban Najeriya rancen da babu kuɗin ruwa ranar Litinin da ta gabata, kamar yadda The Cable ta tattaro.

Ƙarin bayani na nan tafe...

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN