Tsohon IGP Baba ya mikawa Egbetokun shugabancin Yan sandan Najeriya

IGP Kayode Egbetokun

A ranar Larabar da ta gabata ne tsohon Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya, Usman Baba, ya mika ragamar jagorancin rundunar ‘yan sandan Nijeriya ga mukaddashin IGP Kayode Egbetokun.

 An yi bikin mika kayayyakin ne a hedikwatar rundunar da ke Louis Edet House, Abuja. Shafin isyaku.com ya samo.

 Da yake magana, Usman Baba ya ce ya bar rundunar ‘yan sandan Najeriya fiye da yadda ya tarar da ita, ya kuma kara da cewa aikin ‘yan sanda ya kara daraja a Najeriya.

 “Yayin da na fice daga shugabancin rundunar a yau, na yi imanin cewa na bar ta fiye da yadda na same ta.  Na yi imanin cewa na kara darajar aikin 'yan sanda a Najeriya". 

"Ina da yakinin cewa an samu ci gaba mai dorewa a dukkan bangarorin alkawarin da na dauka na sauya labaran aikin 'yan sanda da kuma a tafiyarmu na maido da 'yan sanda bisa hayyacinta nazamar da ingantaccen tsaro ga al'ummar kasar nan".


By/Daga - Click/Latsa isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN