Tinubu ya yi wa yan Najeriya wani albishir bayan cire tallafin man fetur

Bola Ahmed Tinubu the President of Nigeria

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya bada tabbacin cewa ana shirin samar da ababen more rayuwa don dakile illar cire tallafin man fetur.

 Ya yi wannan jawabi ne a yayin wani taron tattaunawa da ‘yan Najeriya mazauna Faransa da makwaftaka da kasashen Turai, a gefen taron sabuwar yarjejeniyar hada-hadar kudade ta duniya da aka yi a babban birnin kasar Faransa, Paris.

 Shugaban a jawabinsa na bude taron ya ce zamanin tallafin ya wuce ne saboda babu kasafi a cikin kasafin kudi. Jaridar The Nation to rahoto.

 Dangane da yadda ya shawo kan kungiyar Labour ta tsayar da zanga-zangar da aka shirya yi kan cire tallafin, ya ce: 

“Kuna son karin kudi a cikin abin dogaro, sufuri me kuke zanga-zangar?  Kuna raba wani É“angare na tallafin?  idan kun yi zanga-zanga ni ma zan bi ku in yi zanga zangar.  Babu zanga-zanga.

 "Za mu samu Palliative amma dole ne mu ajiye kudin domin tanadi," in ji shi.

By/Daga - Click/Latsa isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN