Labari Mai Zafi: EFCC Ta Karyata Zargin Neman Tsohon Gwamnan APC Ruwa a Jallo

Bello Matawalle

Hukumar EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta ayyana Alhaji Bello Matawalle a cikin wadanda ta ke nema. 

Rahoto ya fito daga Tribune cewa EFCC ta na farautar Bello Muhammad Matawalle bisa zargin rashin gaskiya da ya tafka a lokacin ya na ofis.

Bello Muhammad Matawalle ya yi gwamna na shekaru hudud aga 2019 zuwa 2023 a Zamfara. Wani babban jami’in hukumar ya shaidawa Sunday Tribune cewa a ranar Asaba, EFCC ta bukaci DSS ta bada umarnin cafke Bello Matawalle. 

Zuwa yanzu ba mu samu cikakken bayanin laifuffukan da ake tuhumar Matawalle da aikatawa ba.

 EFCC ta na so jami’an hukumar DSS su bada dama a damke tsohon Gwamnan a duk inda aka gan shi a fadin Najeriya domin ayi bincike a kan shi. 

Hakan ya na zuwa ne ‘yan kwanaki kadan bayan shugaban Najeriya ya dakatar da Abdulrasheed Bawa daga kujerar da yake kai na shugaban EFCC. 

Kafin a dakatar da Abdulrasheed Bawa, ya fito fili ya na musayar kalamai da tsohon Gwamnan wanda ya bukaci a dakatar da shi daga bakin aiki. 

By/Daga - Click/Latsa isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN