Yanzu yanzu: Mutane, Motoci da dama sun kone kurmus yayin da tankar mai ta fashe a babbar hanyar Lokoja zuwa Abuja

Illustrative picture

Rahotanni sun ce mutane da dama sun kone kurmus a wani hatsarin da ya faru a hanyar Lokoja zuwa Abuja a jihar Kogi.

 Wani ganau ya ce hatsarin ya faru ne lokacin da wata tankar mai dauke da mai ta rasa yadda za ta yi ta yi karo da motoci daga wata hanya. Daily trust ta rahoto.

 “Tankar na ci gaba da konewa tare da wasu motoci da dama da suka makale a cikin lamarin.  Na ga bas guda biyu na kasuwanci da motoci  suna ci da wuta.  Jami’an tsaro da suka hada da jami’an hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) sun yi namijin kokari wajen kashe gobarar tare da ceto fasinjojin da suka makale a cikin gobarar,” in ji wani Yusuf daga garin kotonkarfei.

 A cewarsa, hadarin ya afku ne kai tsaye a gaban sakatariyar karamar hukumar.

 Kwamandan hukumar kiyaye haddura ta kasa Stephen Dawlung ya shaida wa Daily trust cewa an tura jami’an hukumar zuwa yankin.

 “Mutane da yawa sun makale a hatsarin .  Har yanzu dai tankar na ci gaba da konewa, lamarin da ya haifar da kalubalen zirga-zirgar ababen hawa a kan manyan tituna a halin yanzu.  Zan ba ku cikakkun bayanai, da zarar mun gama,” in ji shugaban FRSC.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN