Type Here to Get Search Results !

Da duminsa: EFCC ta bankado shirin wasu Gwamnoni na tserewa bayan ranar Mayu 29


Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, a jiya ta ce ta bankado shirin da wasu masu rike da mukaman siyasa suka yi na ficewa daga kasar bayan wa’adinsu na ranar 29 ga watan Mayu.

 PEPs sun hada da gwamnoni, ministoci da kuma masu rike da mukaman siyasa da ake sa ido a kansu. Thenation ta rahoto.

 Hukumar ta sake caccakar Gwamna Bello Muhammed Matawalle kan zargin karbar cin hancin dala miliyan 2 da ake alakantawa da shugabanta, Abdulrasheed Bawa.

 Ya bayyana zargin a matsayin yaudara.

A cikin wata sanarwa da shugaban ta na yada labarai Mista Wilson Uwujaren ya fitar, EFCC ta bukaci abokan huldar ta na kasa da kasa da su dakile kubucewar PEPs.

 Sanarwar ta ce: “Haka kuma, hukumar na son sanar da jama’a game da shirye-shiryen da wasu Yan siyasa da ake zargi da cin hanci da rashawa ke yi na ficewa daga kasar nan gabanin ranar 29 ga watan Mayu.

 "Hukumar tana aiki tare da hadin gwiwa tare da takwarorinta na kasa da kasa don dakile wadannan tsare-tsaren tserewa tare da gurfanar da wadanda ke zargi a gaban kotun shari'a."

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN